Connect with us

News in Hausa

Kotu ta ci Tarar Gwamnatin Kano akan Rusau

Published

on

Wata babbar kotun tarayya da ke Kano ta umurci gwamnatin jihar da sauran wadanda aka yi ƙara, su biya wasu mazauna unguwar Salanta, kudi naira miliyan ɗaya kowannensu akan yunƙurin rusa musu kadarori ba bisa ƙa’ida ba.

Alkalin kotun, Mai shari’a Simon Amobeda ya yanke hukuncin cewa yunƙurin gwamnatin Kano da jami’anta na sanya wa gidan Saminu Shehu Muhd ​​da na Tasiu Shehu Muhd ​cikin ​jerin gidajen da za a iya rushewa bayan an buga musu lambar jan fenti ba tare da bin ƙa’ida ba, tauye ƴancinsu ne na mallakar kadara kamar yadda sashe na 43 da 44 na tsarin mulkin Najeriya na 1999 ya tabbatar musu.

Jaridar Daily Trust ta ambato Barista Bashir Ibrahim, wanda ya shigar da karar a madadin Saminu da Tasiu, bayan yanke hukuncin yana yaba wa kotun bisa wannan hukunci, inda ya bayyana hakan a matsayin wata alama ta kare haƙƙi da martaba ƙimar ɗan’adam.

A nasa bangaren, lauyan gwamnatin jihar Kano da sauran waɗanda aka yi ƙara a shari’ar, Barista Musa Dahuru Muhd ​​daraktan shari’a a ma’aikatar shari’a ta Kano ya ce za su yi nazari a kan hukuncin tare da bai wa gwamnati shawara game da mataki na gaba.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

News in Hausa

Kotu za ta yanke hukunci a kan zaben gwamnan Kaduna

Published

on

By

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ke jihar Kaduna za ta yanke hukunci a yau Alhamis 28 ga Satumba, 2023.
Jaridar The Boss ta samu labarin cewa kotun zata zartar da hukuncinta ne ta hanyar Zoom, a inda zata ayyana hukunci kan karar da jam’iyyar PDP da dan takararta, Isah Mohammed Ashiru Kudan suka gabatar a gabanta na neman korar Uba Sani a matsayin gwamnan jihar. Sani ya kasance dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a lokacin zaben.
Jaridar The Boss zata kawo cikakkun bayanai daga baya…

Continue Reading

News in Hausa

Kungiyar Kwadago Zata Shiga Yajin Aikin Sai Baba Tagani

Published

on

By

Kungiyoyin kwadago na NLC da TUC ta sanar da kudirinda na shiga aikin sai baba tagani a ranar Talata mai zuwa 3 ga watan Oktoba 2023. Hakan ya biyo bayan zaman tattaunawa da shugabannin kungiyoyin sukayi a yau Talata a Abuja.
Daya daga cikin korafin kungiyoyin nada alaka da halin tsananin wahala da yan Najeriya suke ciki, da kuma gazawar gwamnatin tarayya bisa alkawarin kawo tsare-tsare na rage radadi ga al’umma.

Continue Reading

News in Hausa

Gwamnan Kano Yusuf Na Jamiyyar NNPP Ya Daukaka Kara

Published

on

By

Gwamnan Jihar Kano, Alh Abba Kabir Yusuf da jamiyyar NNPP sun tafi kotun daukaka kara dake Kaduna domin daukakak kara kan hukuncin da kotun sauraren Korafe-Korafen Zaben gwamna a Jihar Kano ta Yanke a Bisa Kuskure.

Jaridar Boss ta tattaro bayani cewa gwamnatin Kano ta hayo manyan lauyoyi da zasu tsaya Mata a Kotun daukaka Kara da ke Kaduna.

Ga Jerin Gogaggun lauyoyin Masu Rike da Mukamin SAN ( Senior Advocate of Nigeria) Har Guda BAKWAI (7), Ga Jerin Sunayen Su Nan Akasa.

1. Chief Awomolo (SAN)
2. Chief John Beisha (SAN)
3. Chief Lawan Rabbana (SAN)
4. A . J Owonikoko (SAN)
5. Akomolafe (SAN)
6. Abdulhamid Muhammed (SAN)
7. Eyitayo Fatogun (SAN)

Continue Reading

Trending

%d bloggers like this: