A cikin dama guda daya da Gwamnan Ribas Siminalaya Fubara ya samu:
1. Ya kori shugaban ma’aikata na fadar Gwamnatin jihar, wanda Wike ne ya nada shi.
2. Ya cire dukkan shugabannin kananan hukumomi guda ashirin da uku ba jihar baki daya, wanda duk Wike ne ya kawo su.
3. Ya rushe majalisar zartarwar jihar, wadda ta kunshi Kwamishinoni, wanda fiye da rabinsu Wike ne ya kawo su.
4. Ya canja Kakakin Majalisar dokokin jihar wanda shima Wike ne ya kawo shi.
5. Ya dakatar da babban jojin jihar wanda shima Wike ne ya kawo shi.
Wannan karamin misali ne na irin karfin da kujerar Gwamna ta ke da shi a Najeriya. Wike ya manta duk abinda yake yi saboda yana rike da kujerar Gwamnan ne, yau damar da ya samu yayi abinda yaga dama ita wani ya samu ya lalata masa siyasa cikin kankanin lokaci.
Wike ya tarawa kansa abokan fada da yawa, kuma ba zai iya ba. Domin da alama Sim Fubara ya kawo karshen tasirin da Wike yake ganin yana da shi a siyasar Najeriya. Kama-ta-dinu tu-danu.