Connect with us

News in Hausa

Sanata Kawu Sumaila ya ja hankalin Tinubu kan illar yakar Nijer

Published

on

Sanata Abdulrahman Kawu Sumaila na Jam’iyar NNPP mai wakiltar Kano ta kudu ya kasance mai magana da yawun sanatocin arewa tun kwanakin Baya. Bayan kama aiki, kawu ya bayyanawa manema labarai akan matsayar kungiyar sanatocin arewa kan maganar da ECOWAS suke akan yakar jamhuriyar Nijer.

Sanata Kawu yace “Mu sanatocin arewa bama goyon bayan yakar jamhuriyar Nijer, kuma muna kira ga ECOWAS karkashin jagorancin shugaba Tinubu da ayi wannan abun cikin masalaha amma bah Yaki bah. Domin Yaki bah Alkhairi bane, Zai Janyo asarar rayuka da dukiyar al’umma wadanda basuji ba basu gani ba.

Haka zalika, jihohin arewacin Najeriya bakwai (7) ne sukayi makokantaka da jamhuryar Nijer kamar Haka:
KATSINA, ZAMFARA, SOKOTO, KEBBI, YOBE, BORNO da JIGAWA.

Duk wannan jihohin Arewacin Najeriya ne, kuma muddin za ayi yaki da kasar Nijer sai al’ummar jihohin sun cutu ta fannoni da dama. Daman chan wasu daga ciki suna fama da rashin tsaro, kaga kenan za’a rura wutar rashin tsaro a wannan yankunan…”
Sanata Kawu Sumaila dai tsohon dan majalisar wakilai ne kwararre wanda ya wakilci kananan hukumomin Sumaila da Takai kuma tsohon mai bawa tsohon shugan kasa Muhammadu Buhari shawara kan abunda ya shafi majalisar.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

News in Hausa

Kotu za ta yanke hukunci a kan zaben gwamnan Kaduna

Published

on

By

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ke jihar Kaduna za ta yanke hukunci a yau Alhamis 28 ga Satumba, 2023.
Jaridar The Boss ta samu labarin cewa kotun zata zartar da hukuncinta ne ta hanyar Zoom, a inda zata ayyana hukunci kan karar da jam’iyyar PDP da dan takararta, Isah Mohammed Ashiru Kudan suka gabatar a gabanta na neman korar Uba Sani a matsayin gwamnan jihar. Sani ya kasance dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a lokacin zaben.
Jaridar The Boss zata kawo cikakkun bayanai daga baya…

Continue Reading

News in Hausa

Kungiyar Kwadago Zata Shiga Yajin Aikin Sai Baba Tagani

Published

on

By

Kungiyoyin kwadago na NLC da TUC ta sanar da kudirinda na shiga aikin sai baba tagani a ranar Talata mai zuwa 3 ga watan Oktoba 2023. Hakan ya biyo bayan zaman tattaunawa da shugabannin kungiyoyin sukayi a yau Talata a Abuja.
Daya daga cikin korafin kungiyoyin nada alaka da halin tsananin wahala da yan Najeriya suke ciki, da kuma gazawar gwamnatin tarayya bisa alkawarin kawo tsare-tsare na rage radadi ga al’umma.

Continue Reading

News in Hausa

Gwamnan Kano Yusuf Na Jamiyyar NNPP Ya Daukaka Kara

Published

on

By

Gwamnan Jihar Kano, Alh Abba Kabir Yusuf da jamiyyar NNPP sun tafi kotun daukaka kara dake Kaduna domin daukakak kara kan hukuncin da kotun sauraren Korafe-Korafen Zaben gwamna a Jihar Kano ta Yanke a Bisa Kuskure.

Jaridar Boss ta tattaro bayani cewa gwamnatin Kano ta hayo manyan lauyoyi da zasu tsaya Mata a Kotun daukaka Kara da ke Kaduna.

Ga Jerin Gogaggun lauyoyin Masu Rike da Mukamin SAN ( Senior Advocate of Nigeria) Har Guda BAKWAI (7), Ga Jerin Sunayen Su Nan Akasa.

1. Chief Awomolo (SAN)
2. Chief John Beisha (SAN)
3. Chief Lawan Rabbana (SAN)
4. A . J Owonikoko (SAN)
5. Akomolafe (SAN)
6. Abdulhamid Muhammed (SAN)
7. Eyitayo Fatogun (SAN)

Continue Reading

Trending

%d bloggers like this: