Sanata Kawu Sumaila ya ja hankalin Tinubu kan illar yakar Nijer

Date:

Sanata Abdulrahman Kawu Sumaila na Jam’iyar NNPP mai wakiltar Kano ta kudu ya kasance mai magana da yawun sanatocin arewa tun kwanakin Baya. Bayan kama aiki, kawu ya bayyanawa manema labarai akan matsayar kungiyar sanatocin arewa kan maganar da ECOWAS suke akan yakar jamhuriyar Nijer.

Sanata Kawu yace “Mu sanatocin arewa bama goyon bayan yakar jamhuriyar Nijer, kuma muna kira ga ECOWAS karkashin jagorancin shugaba Tinubu da ayi wannan abun cikin masalaha amma bah Yaki bah. Domin Yaki bah Alkhairi bane, Zai Janyo asarar rayuka da dukiyar al’umma wadanda basuji ba basu gani ba.

Haka zalika, jihohin arewacin Najeriya bakwai (7) ne sukayi makokantaka da jamhuryar Nijer kamar Haka:
KATSINA, ZAMFARA, SOKOTO, KEBBI, YOBE, BORNO da JIGAWA.

Duk wannan jihohin Arewacin Najeriya ne, kuma muddin za ayi yaki da kasar Nijer sai al’ummar jihohin sun cutu ta fannoni da dama. Daman chan wasu daga ciki suna fama da rashin tsaro, kaga kenan za’a rura wutar rashin tsaro a wannan yankunan…”
Sanata Kawu Sumaila dai tsohon dan majalisar wakilai ne kwararre wanda ya wakilci kananan hukumomin Sumaila da Takai kuma tsohon mai bawa tsohon shugan kasa Muhammadu Buhari shawara kan abunda ya shafi majalisar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

spot_imgspot_img

Popular

More like this
Related

UK PM Burnham Unveils 10-Year Plan, Begins Cabinet Overhaul

The new British Prime Minister, Andy Burnham, on Monday,...

Where’s the Nigeria’s Oil Metering Fund?

By Boma Lilian Braide Esq A single administrative letter dated...

ADC Tells Tinubu to Resign As World Bank Reveals 139million Nigerians Live in Poverty

The African Democratic Congress (ADC) on Saturday asked President...

Dominican University Hails Peter Obi on 65th Birthday

The Dominican University, Ibadan, has paid glowing tribute to...