Shugaba Bola Tinubu ya shirya aika jerin sunayen ministoci na biyu ga majalisar dattawa domin tantancewa a yau, kamar yadda wata majiya mai tushe a cikin majalisar ta bayyanawa Jaridar Boss.
A cewar majiyar, za a gabatar da sabbin rukunin ministocin da aka nada a yayin zaman najalisa na yau Laraba.
Kamar yadda jaridar Punch itama ta ruwaito, majiyar ta ce ” Zuwa ranar Laraba, za a fitar da sabbin sunayen wadanda aka nada, ta yadda zuwa ranar Litinin za su ci gaba da tantance su.”
Ana sa ran kammala aikin tantance mutane 28 da aka zaba cikin gaggawa, wanda zai ba da damar tantance rukunin wadanda za a tantance daga baya.


