Connect with us

News in Hausa

Tinubu zai aika jerin sunayen ministoci kashi na biyu a yau

Published

on

Shugaba Bola Tinubu ya shirya aika jerin sunayen ministoci na biyu ga majalisar dattawa domin tantancewa a yau, kamar yadda wata majiya mai tushe a cikin majalisar ta bayyanawa Jaridar Boss.

A cewar majiyar, za a gabatar da sabbin rukunin ministocin da aka nada a yayin zaman najalisa na yau Laraba.

Kamar yadda jaridar Punch itama ta ruwaito, majiyar ta ce ” Zuwa ranar Laraba, za a fitar da sabbin sunayen wadanda aka nada, ta yadda zuwa ranar Litinin za su ci gaba da tantance su.”

Ana sa ran kammala aikin tantance mutane 28 da aka zaba cikin gaggawa, wanda zai ba da damar tantance rukunin wadanda za a tantance daga baya.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

News in Hausa

Kotu za ta yanke hukunci a kan zaben gwamnan Kaduna

Published

on

By

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ke jihar Kaduna za ta yanke hukunci a yau Alhamis 28 ga Satumba, 2023.
Jaridar The Boss ta samu labarin cewa kotun zata zartar da hukuncinta ne ta hanyar Zoom, a inda zata ayyana hukunci kan karar da jam’iyyar PDP da dan takararta, Isah Mohammed Ashiru Kudan suka gabatar a gabanta na neman korar Uba Sani a matsayin gwamnan jihar. Sani ya kasance dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a lokacin zaben.
Jaridar The Boss zata kawo cikakkun bayanai daga baya…

Continue Reading

News in Hausa

Kungiyar Kwadago Zata Shiga Yajin Aikin Sai Baba Tagani

Published

on

By

Kungiyoyin kwadago na NLC da TUC ta sanar da kudirinda na shiga aikin sai baba tagani a ranar Talata mai zuwa 3 ga watan Oktoba 2023. Hakan ya biyo bayan zaman tattaunawa da shugabannin kungiyoyin sukayi a yau Talata a Abuja.
Daya daga cikin korafin kungiyoyin nada alaka da halin tsananin wahala da yan Najeriya suke ciki, da kuma gazawar gwamnatin tarayya bisa alkawarin kawo tsare-tsare na rage radadi ga al’umma.

Continue Reading

News in Hausa

Gwamnan Kano Yusuf Na Jamiyyar NNPP Ya Daukaka Kara

Published

on

By

Gwamnan Jihar Kano, Alh Abba Kabir Yusuf da jamiyyar NNPP sun tafi kotun daukaka kara dake Kaduna domin daukakak kara kan hukuncin da kotun sauraren Korafe-Korafen Zaben gwamna a Jihar Kano ta Yanke a Bisa Kuskure.

Jaridar Boss ta tattaro bayani cewa gwamnatin Kano ta hayo manyan lauyoyi da zasu tsaya Mata a Kotun daukaka Kara da ke Kaduna.

Ga Jerin Gogaggun lauyoyin Masu Rike da Mukamin SAN ( Senior Advocate of Nigeria) Har Guda BAKWAI (7), Ga Jerin Sunayen Su Nan Akasa.

1. Chief Awomolo (SAN)
2. Chief John Beisha (SAN)
3. Chief Lawan Rabbana (SAN)
4. A . J Owonikoko (SAN)
5. Akomolafe (SAN)
6. Abdulhamid Muhammed (SAN)
7. Eyitayo Fatogun (SAN)

Continue Reading

Trending

%d bloggers like this: