Connect with us

News in Hausa

Tinubu zai aika jerin sunayen ministoci kashi na biyu a yau

Published

on

Shugaba Bola Tinubu ya shirya aika jerin sunayen ministoci na biyu ga majalisar dattawa domin tantancewa a yau, kamar yadda wata majiya mai tushe a cikin majalisar ta bayyanawa Jaridar Boss.

A cewar majiyar, za a gabatar da sabbin rukunin ministocin da aka nada a yayin zaman najalisa na yau Laraba.

Kamar yadda jaridar Punch itama ta ruwaito, majiyar ta ce ” Zuwa ranar Laraba, za a fitar da sabbin sunayen wadanda aka nada, ta yadda zuwa ranar Litinin za su ci gaba da tantance su.”

Ana sa ran kammala aikin tantance mutane 28 da aka zaba cikin gaggawa, wanda zai ba da damar tantance rukunin wadanda za a tantance daga baya.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

News in Hausa

Shin ko karfin siyasar ta Wike tasamu rauni?

Published

on

By

A cikin dama guda daya da Gwamnan Ribas Siminalaya Fubara ya samu:

1. Ya kori shugaban ma’aikata na fadar Gwamnatin jihar, wanda Wike ne ya nada shi.

2. Ya cire dukkan shugabannin kananan hukumomi guda ashirin da uku ba jihar baki daya, wanda duk Wike ne ya kawo su.

3. Ya rushe majalisar zartarwar jihar, wadda ta kunshi Kwamishinoni, wanda fiye da rabinsu Wike ne ya kawo su.

4. Ya canja Kakakin Majalisar dokokin jihar wanda shima Wike ne ya kawo shi.

5. Ya dakatar da babban jojin jihar wanda shima Wike ne ya kawo shi.

Wannan karamin misali ne na irin karfin da kujerar Gwamna ta ke da shi a Najeriya. Wike ya manta duk abinda yake yi saboda yana rike da kujerar Gwamnan ne, yau damar da ya samu yayi abinda yaga dama ita wani ya samu ya lalata masa siyasa cikin kankanin lokaci.

Wike ya tarawa kansa abokan fada da yawa, kuma ba zai iya ba. Domin da alama Sim Fubara ya kawo karshen tasirin da Wike yake ganin yana da shi a siyasar Najeriya. Kama-ta-dinu tu-danu.

Continue Reading

News in Hausa

Kotu za ta yanke hukunci a kan zaben gwamnan Kaduna

Published

on

By

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ke jihar Kaduna za ta yanke hukunci a yau Alhamis 28 ga Satumba, 2023.
Jaridar The Boss ta samu labarin cewa kotun zata zartar da hukuncinta ne ta hanyar Zoom, a inda zata ayyana hukunci kan karar da jam’iyyar PDP da dan takararta, Isah Mohammed Ashiru Kudan suka gabatar a gabanta na neman korar Uba Sani a matsayin gwamnan jihar. Sani ya kasance dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a lokacin zaben.
Jaridar The Boss zata kawo cikakkun bayanai daga baya…

Continue Reading

News in Hausa

Kungiyar Kwadago Zata Shiga Yajin Aikin Sai Baba Tagani

Published

on

By

Kungiyoyin kwadago na NLC da TUC ta sanar da kudirinda na shiga aikin sai baba tagani a ranar Talata mai zuwa 3 ga watan Oktoba 2023. Hakan ya biyo bayan zaman tattaunawa da shugabannin kungiyoyin sukayi a yau Talata a Abuja.
Daya daga cikin korafin kungiyoyin nada alaka da halin tsananin wahala da yan Najeriya suke ciki, da kuma gazawar gwamnatin tarayya bisa alkawarin kawo tsare-tsare na rage radadi ga al’umma.

Continue Reading

Trending