Zanga-zangar da kungiyar kwadago ta shirya a yau Laraba ta nuna adawa ga manufofin gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu musamman kan janye tallafin man fetur na kara zafi yayin da masu zanga-zangar a yau Laraba, da safe suka fasa kofar farko na harabar majalisar dokokin kasar tare da yunkurin shiga harabar. Daga bisani kuma aka koma kofar dakin taro na biyu na Majalisar. Kungiyoyin kwadagon da suka hada da Nigerian Labour Congress (NLC), Trade Union Congress (TUC) da sauran kungiyoyinsu, a yau, sun fara wata zanga-zanga a babban birnin tarayya Abuja (FCT), da sauran jihohin tarayyar da suka hada da Legas, Abia, Plateau, Kaduna, Kano, Rivers, Zamfara, Katsina, Cross River, Ebonyi, Enugu, Kwara, Ogun, Imo, Ondo, da Edo.
Masu zanga-zangar a daruruwansu sun yi taro a wurin taron Unity Fountain daga inda suka yi tattaki zuwa dakin taro na NASS. Ana sa ran shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio zai yi jawabi ga masu zanga-zangar gabanin tantance sunayen ministocin da za a yi a yau.


