Connect with us

News in Hausa

Cire tallafin man fetur: Jihohi da Kananan Hukumomin Najeriya Zasu Samu kaso mai tsoka a watan Yuli

Published

on

Kwamitin raba KUDADEN hadaka na kasa zai raba kimanin naira tiriliyan 2 a watan Yuli, karo na farko a tarihi, a matsayin kason da matakai uku na gwamnati za su samu a matsayin rabon su,. Sakamakon cire tallafin man fetir da a ka yi.

Wannan dumbin kudi da, da ba a cire tallafin ba, zai salwanta a wancan 6angare a wata daya, yanzu zai tafi zuwa ga inganta rayuwar al’umma.

Gwamnatocin jihohi da na kananan hukumomi yanzu za su samu wadatattun kudi da za su biya albashin maaikatan su da Kuma ‘yan fansho. Gwamnatocin za su zama masu wadatar da zasu rage kar6i bashi, Kuma za su iya biyan mafi kankantar albashi Kuma su bayar da isassun kudaden da za a tabbatar da ci gaba a 6angarorin ilimi, lafiya da sifiri.

Duba da wannan, dole yanzu a saka Ido a Kan gwamnatocin jihohi da kananan hukumomi domin tabbatar da gaskiya da amana wajen gudanar da dukiyar al’umma. Gudanarwa ingantacciya tana da muhimmanci a matakin jihohi da kananan hukumomi.

Rahotanni sun nuna cewa daga wannan adadi na naira tiriliyan 2, kusan naira tiriliyan 1 za a rabawa matakan gwamnati guda 3, ragowar tiriliyan daya za a saka su a wani sabon asusu da za a Rika amfani da su wajen gudanar da ayyukan bai daya da zasu rage radadin da cire tallafin man fetir ya gadar wa da talakawa.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

News in Hausa

Kotu za ta yanke hukunci a kan zaben gwamnan Kaduna

Published

on

By

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ke jihar Kaduna za ta yanke hukunci a yau Alhamis 28 ga Satumba, 2023.
Jaridar The Boss ta samu labarin cewa kotun zata zartar da hukuncinta ne ta hanyar Zoom, a inda zata ayyana hukunci kan karar da jam’iyyar PDP da dan takararta, Isah Mohammed Ashiru Kudan suka gabatar a gabanta na neman korar Uba Sani a matsayin gwamnan jihar. Sani ya kasance dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a lokacin zaben.
Jaridar The Boss zata kawo cikakkun bayanai daga baya…

Continue Reading

News in Hausa

Kungiyar Kwadago Zata Shiga Yajin Aikin Sai Baba Tagani

Published

on

By

Kungiyoyin kwadago na NLC da TUC ta sanar da kudirinda na shiga aikin sai baba tagani a ranar Talata mai zuwa 3 ga watan Oktoba 2023. Hakan ya biyo bayan zaman tattaunawa da shugabannin kungiyoyin sukayi a yau Talata a Abuja.
Daya daga cikin korafin kungiyoyin nada alaka da halin tsananin wahala da yan Najeriya suke ciki, da kuma gazawar gwamnatin tarayya bisa alkawarin kawo tsare-tsare na rage radadi ga al’umma.

Continue Reading

News in Hausa

Gwamnan Kano Yusuf Na Jamiyyar NNPP Ya Daukaka Kara

Published

on

By

Gwamnan Jihar Kano, Alh Abba Kabir Yusuf da jamiyyar NNPP sun tafi kotun daukaka kara dake Kaduna domin daukakak kara kan hukuncin da kotun sauraren Korafe-Korafen Zaben gwamna a Jihar Kano ta Yanke a Bisa Kuskure.

Jaridar Boss ta tattaro bayani cewa gwamnatin Kano ta hayo manyan lauyoyi da zasu tsaya Mata a Kotun daukaka Kara da ke Kaduna.

Ga Jerin Gogaggun lauyoyin Masu Rike da Mukamin SAN ( Senior Advocate of Nigeria) Har Guda BAKWAI (7), Ga Jerin Sunayen Su Nan Akasa.

1. Chief Awomolo (SAN)
2. Chief John Beisha (SAN)
3. Chief Lawan Rabbana (SAN)
4. A . J Owonikoko (SAN)
5. Akomolafe (SAN)
6. Abdulhamid Muhammed (SAN)
7. Eyitayo Fatogun (SAN)

Continue Reading

Trending

%d bloggers like this: