Da Dumi Dumi: Majalisar dattawa sunki amincewa da Tinubu ya tura Sojoji Nijar
Majalisar Dattawa ta ki amincewa da bukatar Tinubu na tura sojoji Nijar. Majalisar ta bukaci shugaban kungiyar ECOWAS da sauran shugabannin yankin da su yi taka-tsan-tsan wajen magance tabarbarewar siyasar a Jamhuriyar Nijar musamman ma ga me da juyin mulki da soji sukayi a sati da ya gabata.
A wani zama na sirri da ya dauki kusan sa’o’i biyu ana tattaunawa kan wasikar da shugaban kasa Bola Tinubu ya rubutawa majalisar dattawa a ranar Juma’a kan shawarar da kungiyar yankin ta dauka, majalisar ta bukaci kungiyar ECOWAS da ta karfafa zabin siya sa da diflomasiyya da sauran hanyoyin sasantawa.


