Connect with us

News in Hausa

Dalilin da yasa Osinbajo bai halarci taron jam’iyyar APC ba

Published

on

Laolu Akande, mai magana da yawun tsohon mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya bayyana dalilin rashin halartar tsohon mataimakin shugaban kasa a taron jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

A cikin wata sanarwa da Akande ya fitar, ya ce Osinbajo ba zai iya halartar taron ba a ranar Larabar da ta gabata, saboda yayi balaguru wajen Najeriya ne saboda wasu ayyuka da ya sa a gaba.

“A cikin wasikar neman gafara saboda rashin zuwansa da ya aike wa mukaddashin shugaban jam’iyyar (Abubakar Kyari), tsohon mataimakin shugaban kasar ya bayyana cewa ya riga ya fita kasar waje domin wasu muhimman ayyuka, a lokacin da ya samu gayyatar taron. ”

Bayanin a wani bangare ya zo kamar haka:

“Hakika ya soke wasu alkawurran da ya yi a kasashen waje domin halartar tarukan jiga-jigan jam’iyyar guda biyu da aka shirya a baya wadanda daga bisani aka dage su.

“Yayin da yake yi wa jam’iyyar fatan alkhairi, ya bayyana kudurinsa na bawa jam’iyyar cikakken goyon baya da kuma samun halartar tarurruka da ayyukan jam’iyyar nan gaba.”

Osinbajo ya kasance mataimakin shugaban Najeriya daga watan Mayu na shekarar 2015 zuwa Mayu 2023 a lokacin gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Farfesan lauyan ya tsaya takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC a watan Yunin 2022 amma ya sha kaye a hannun tsohon gwamnan jihar Legas, Bola Tinubu.

Wani abin sha’awa shi ne, Osinbajo ya kasance daya daga cikin manyan lauyoyi na yankin Yorubawa kuma kwamishinan shari’a na Legas a lokacin da Tinubu yake gwamnan Legas tsakanin 1999 zuwa 2007.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

News in Hausa

Shin ko karfin siyasar ta Wike tasamu rauni?

Published

on

By

A cikin dama guda daya da Gwamnan Ribas Siminalaya Fubara ya samu:

1. Ya kori shugaban ma’aikata na fadar Gwamnatin jihar, wanda Wike ne ya nada shi.

2. Ya cire dukkan shugabannin kananan hukumomi guda ashirin da uku ba jihar baki daya, wanda duk Wike ne ya kawo su.

3. Ya rushe majalisar zartarwar jihar, wadda ta kunshi Kwamishinoni, wanda fiye da rabinsu Wike ne ya kawo su.

4. Ya canja Kakakin Majalisar dokokin jihar wanda shima Wike ne ya kawo shi.

5. Ya dakatar da babban jojin jihar wanda shima Wike ne ya kawo shi.

Wannan karamin misali ne na irin karfin da kujerar Gwamna ta ke da shi a Najeriya. Wike ya manta duk abinda yake yi saboda yana rike da kujerar Gwamnan ne, yau damar da ya samu yayi abinda yaga dama ita wani ya samu ya lalata masa siyasa cikin kankanin lokaci.

Wike ya tarawa kansa abokan fada da yawa, kuma ba zai iya ba. Domin da alama Sim Fubara ya kawo karshen tasirin da Wike yake ganin yana da shi a siyasar Najeriya. Kama-ta-dinu tu-danu.

Continue Reading

News in Hausa

Kotu za ta yanke hukunci a kan zaben gwamnan Kaduna

Published

on

By

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ke jihar Kaduna za ta yanke hukunci a yau Alhamis 28 ga Satumba, 2023.
Jaridar The Boss ta samu labarin cewa kotun zata zartar da hukuncinta ne ta hanyar Zoom, a inda zata ayyana hukunci kan karar da jam’iyyar PDP da dan takararta, Isah Mohammed Ashiru Kudan suka gabatar a gabanta na neman korar Uba Sani a matsayin gwamnan jihar. Sani ya kasance dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a lokacin zaben.
Jaridar The Boss zata kawo cikakkun bayanai daga baya…

Continue Reading

News in Hausa

Kungiyar Kwadago Zata Shiga Yajin Aikin Sai Baba Tagani

Published

on

By

Kungiyoyin kwadago na NLC da TUC ta sanar da kudirinda na shiga aikin sai baba tagani a ranar Talata mai zuwa 3 ga watan Oktoba 2023. Hakan ya biyo bayan zaman tattaunawa da shugabannin kungiyoyin sukayi a yau Talata a Abuja.
Daya daga cikin korafin kungiyoyin nada alaka da halin tsananin wahala da yan Najeriya suke ciki, da kuma gazawar gwamnatin tarayya bisa alkawarin kawo tsare-tsare na rage radadi ga al’umma.

Continue Reading

Trending