Connect with us

News in Hausa

Dalilin da yasa Osinbajo bai halarci taron jam’iyyar APC ba

Published

on

Laolu Akande, mai magana da yawun tsohon mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya bayyana dalilin rashin halartar tsohon mataimakin shugaban kasa a taron jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

A cikin wata sanarwa da Akande ya fitar, ya ce Osinbajo ba zai iya halartar taron ba a ranar Larabar da ta gabata, saboda yayi balaguru wajen Najeriya ne saboda wasu ayyuka da ya sa a gaba.

“A cikin wasikar neman gafara saboda rashin zuwansa da ya aike wa mukaddashin shugaban jam’iyyar (Abubakar Kyari), tsohon mataimakin shugaban kasar ya bayyana cewa ya riga ya fita kasar waje domin wasu muhimman ayyuka, a lokacin da ya samu gayyatar taron. ”

Bayanin a wani bangare ya zo kamar haka:

“Hakika ya soke wasu alkawurran da ya yi a kasashen waje domin halartar tarukan jiga-jigan jam’iyyar guda biyu da aka shirya a baya wadanda daga bisani aka dage su.

“Yayin da yake yi wa jam’iyyar fatan alkhairi, ya bayyana kudurinsa na bawa jam’iyyar cikakken goyon baya da kuma samun halartar tarurruka da ayyukan jam’iyyar nan gaba.”

Osinbajo ya kasance mataimakin shugaban Najeriya daga watan Mayu na shekarar 2015 zuwa Mayu 2023 a lokacin gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Farfesan lauyan ya tsaya takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC a watan Yunin 2022 amma ya sha kaye a hannun tsohon gwamnan jihar Legas, Bola Tinubu.

Wani abin sha’awa shi ne, Osinbajo ya kasance daya daga cikin manyan lauyoyi na yankin Yorubawa kuma kwamishinan shari’a na Legas a lokacin da Tinubu yake gwamnan Legas tsakanin 1999 zuwa 2007.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

News in Hausa

Kotu za ta yanke hukunci a kan zaben gwamnan Kaduna

Published

on

By

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ke jihar Kaduna za ta yanke hukunci a yau Alhamis 28 ga Satumba, 2023.
Jaridar The Boss ta samu labarin cewa kotun zata zartar da hukuncinta ne ta hanyar Zoom, a inda zata ayyana hukunci kan karar da jam’iyyar PDP da dan takararta, Isah Mohammed Ashiru Kudan suka gabatar a gabanta na neman korar Uba Sani a matsayin gwamnan jihar. Sani ya kasance dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a lokacin zaben.
Jaridar The Boss zata kawo cikakkun bayanai daga baya…

Continue Reading

News in Hausa

Kungiyar Kwadago Zata Shiga Yajin Aikin Sai Baba Tagani

Published

on

By

Kungiyoyin kwadago na NLC da TUC ta sanar da kudirinda na shiga aikin sai baba tagani a ranar Talata mai zuwa 3 ga watan Oktoba 2023. Hakan ya biyo bayan zaman tattaunawa da shugabannin kungiyoyin sukayi a yau Talata a Abuja.
Daya daga cikin korafin kungiyoyin nada alaka da halin tsananin wahala da yan Najeriya suke ciki, da kuma gazawar gwamnatin tarayya bisa alkawarin kawo tsare-tsare na rage radadi ga al’umma.

Continue Reading

News in Hausa

Gwamnan Kano Yusuf Na Jamiyyar NNPP Ya Daukaka Kara

Published

on

By

Gwamnan Jihar Kano, Alh Abba Kabir Yusuf da jamiyyar NNPP sun tafi kotun daukaka kara dake Kaduna domin daukakak kara kan hukuncin da kotun sauraren Korafe-Korafen Zaben gwamna a Jihar Kano ta Yanke a Bisa Kuskure.

Jaridar Boss ta tattaro bayani cewa gwamnatin Kano ta hayo manyan lauyoyi da zasu tsaya Mata a Kotun daukaka Kara da ke Kaduna.

Ga Jerin Gogaggun lauyoyin Masu Rike da Mukamin SAN ( Senior Advocate of Nigeria) Har Guda BAKWAI (7), Ga Jerin Sunayen Su Nan Akasa.

1. Chief Awomolo (SAN)
2. Chief John Beisha (SAN)
3. Chief Lawan Rabbana (SAN)
4. A . J Owonikoko (SAN)
5. Akomolafe (SAN)
6. Abdulhamid Muhammed (SAN)
7. Eyitayo Fatogun (SAN)

Continue Reading

Trending

%d bloggers like this: