Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa ya kare tallafin Naira 8,000 da Gwamnatin Tarayya ke shirin kawowa don rage radadin cire tallafin man fetur a tsakanin talakawa.
Da yake magana a gidan Talabijin na Channels sashen siyasa a jiya Juma’a, Gwamnan ya ce N8,000 wani adadi ne mai yawa ga iyalai da dama da ke fama da talauci wadanda ba kasafai ake samun irin wannan ba a cikin wata guda.
Ya tunatar da cewa iyalai da yawa ne suka ci gajiyar N5,000 da aka raba a baya a matsayin agaji, yana mai cewa matakin na yanzu ya dace.
“Muna raba N5,000 ne kawai kuma na yarda cewa akwai mutane da yawa da ke jiran wannan N5,000 duk wata. Lallai akwai wasu al’ummomi da suka iya ba da gudummawarsu kuma sun iya yin abubuwa da yawa a cikin al’ummominsu daban-daban.”
“Don haka, Naira 8,000 na iya zama ba kudi mai yawa ba ga wasu mutane, amma yana da yawa ga wasu da yawa daga cikin iyalai marasa galihu da ba sa ganin N8,000 duk wata. Don haka, abu daya kawai shi ne mu tantance wadannan iyalai.”
Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin sake duba kudaden tallafin Naira 8,000, biyo bayan harzuka da aka yi a fadin kasar.


