Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben ranar 25 ga watan Fabrairu, Alhaji Atiku Abubakar, ya shaida wa kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa (PEPC) da ta bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben bisa la’akari da gabatar da karar da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta yi na cewa ya lashe jihohi 21 a lokacin zaben.
Atiku, a jawabinsa na karshe a rubuce ta hannun lauyoyinsa, ya yi ikirarin cewa hukumar ba ta yi jayayya ba, ko janyewa, ko kuma ta yi ikirarin cewa an tafka kuskure wajen bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben a jihohi 21 ba.
Hakazalika ya roki kotu da ta soke bayyana dan takarar jamiyyar APC Bola Tinubu da hukumar zabe tayi a matsayin wanda ya lashe zaben saboda ya kasa samun kashi daya bisa hudu na kuri’un da aka kada a babban birnin tarayya Abuja.
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Mista Peter Obi, shima ya yi tsokaci a kan irin wannan matsayi.
Ya kara da cewa sashe na 134(2) na kundin tsarin mulkin kasar ya fito karara kan batun samun akalla kashi 25 na kuri’u a babban birnin tarayya Abuja da jihohi 24 a matsayin sharadi na tsayawa takarar shugaban kasa a Najeriya.


