Atiku Ya Nemi Kotu da ta ayyana shi a matsayin Wanda ya Lashe Zaben Shugaban Kasa

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben ranar 25 ga watan Fabrairu, Alhaji Atiku Abubakar, ya shaida wa kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa (PEPC) da ta bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben bisa la’akari da gabatar da karar da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta yi na cewa ya lashe jihohi 21 a lokacin zaben.

Atiku, a jawabinsa na karshe a rubuce ta hannun lauyoyinsa, ya yi ikirarin cewa hukumar ba ta yi jayayya ba, ko janyewa, ko kuma ta yi ikirarin cewa an tafka kuskure wajen bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben a jihohi 21 ba.
Hakazalika ya roki kotu da ta soke bayyana dan takarar jamiyyar APC Bola Tinubu da hukumar zabe tayi a matsayin wanda ya lashe zaben saboda ya kasa samun kashi daya bisa hudu na kuri’un da aka kada a babban birnin tarayya Abuja.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Mista Peter Obi, shima ya yi tsokaci a kan irin wannan matsayi.

Ya kara da cewa sashe na 134(2) na kundin tsarin mulkin kasar ya fito karara kan batun samun akalla kashi 25 na kuri’u a babban birnin tarayya Abuja da jihohi 24 a matsayin sharadi na tsayawa takarar shugaban kasa a Najeriya.

Share post:

Subscribe

spot_imgspot_img

Popular

More like this
Related

Anambra Bizman Abductors Demand N1.5bn Ransom

Gunmen who kidnapped the chairman of Jezco Group, Chief...

State Police Bill: FG Extends Deadline, Seeks More Consultation

The Federal government has extended the deadline for the...

Osun Govt Drags Fadahunsi to Court over “Kill Accord Members” Threat

The Osun State Government has approached the High Court...

Friday Sermon: Talking About the Revolution: The Rise of the Masses

By Babatunde Jose “The children of the poor you failed...