Connect with us

News in Hausa

Yan Majalisar Dattijan Najariya Na Ganawar Sirri Kan Sabbin Ministoci

Published

on

Majalisar Dattijai a halin yanzu na Ganawar Sirri Akan jerin sunayen Sababbin Ministoci da shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya turamusu domin su tantance su a karkashin jagorancin shugaban Majalisar Dattijai Sanata Godswill Akpabio.
Sun Fara tattaunawar da misalin karfe 11:59 a.m bayan Sanata Opeyemi (APC, Ekiti ta tsakiya) Bamidele ya bada sanarwar umarnin.

Wata majiya Mai karfi tayi nuni ga Boss Newspaper Hausa cewa jerin sunayen ya janyo kace-nace tsakanin sanatocin, Wanda hakan ya jawo bukar tattaunawar ta gaggawa a tsakaninsu.

Zamu iya tinawa a jiya Laraba ba shugaban Majalisar Sanata Akpabio yayi wata ganawa Mai tsayi da masu ruwa da tsaki akan al’amarin.

Majiyar ta yi nuni da cewa tuni jerin sunayen yana tare da shugaban Majalisar, inda ake zaton zai karantosu bayan wannan tattaunawa da sukeyi kokuma sati mai zuwa kasancewar babu zaman majalisar a gobe Juma’a.

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

News in Hausa

Kotu za ta yanke hukunci a kan zaben gwamnan Kaduna

Published

on

By

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ke jihar Kaduna za ta yanke hukunci a yau Alhamis 28 ga Satumba, 2023.
Jaridar The Boss ta samu labarin cewa kotun zata zartar da hukuncinta ne ta hanyar Zoom, a inda zata ayyana hukunci kan karar da jam’iyyar PDP da dan takararta, Isah Mohammed Ashiru Kudan suka gabatar a gabanta na neman korar Uba Sani a matsayin gwamnan jihar. Sani ya kasance dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a lokacin zaben.
Jaridar The Boss zata kawo cikakkun bayanai daga baya…

Continue Reading

News in Hausa

Kungiyar Kwadago Zata Shiga Yajin Aikin Sai Baba Tagani

Published

on

By

Kungiyoyin kwadago na NLC da TUC ta sanar da kudirinda na shiga aikin sai baba tagani a ranar Talata mai zuwa 3 ga watan Oktoba 2023. Hakan ya biyo bayan zaman tattaunawa da shugabannin kungiyoyin sukayi a yau Talata a Abuja.
Daya daga cikin korafin kungiyoyin nada alaka da halin tsananin wahala da yan Najeriya suke ciki, da kuma gazawar gwamnatin tarayya bisa alkawarin kawo tsare-tsare na rage radadi ga al’umma.

Continue Reading

News in Hausa

Gwamnan Kano Yusuf Na Jamiyyar NNPP Ya Daukaka Kara

Published

on

By

Gwamnan Jihar Kano, Alh Abba Kabir Yusuf da jamiyyar NNPP sun tafi kotun daukaka kara dake Kaduna domin daukakak kara kan hukuncin da kotun sauraren Korafe-Korafen Zaben gwamna a Jihar Kano ta Yanke a Bisa Kuskure.

Jaridar Boss ta tattaro bayani cewa gwamnatin Kano ta hayo manyan lauyoyi da zasu tsaya Mata a Kotun daukaka Kara da ke Kaduna.

Ga Jerin Gogaggun lauyoyin Masu Rike da Mukamin SAN ( Senior Advocate of Nigeria) Har Guda BAKWAI (7), Ga Jerin Sunayen Su Nan Akasa.

1. Chief Awomolo (SAN)
2. Chief John Beisha (SAN)
3. Chief Lawan Rabbana (SAN)
4. A . J Owonikoko (SAN)
5. Akomolafe (SAN)
6. Abdulhamid Muhammed (SAN)
7. Eyitayo Fatogun (SAN)

Continue Reading

Trending

%d bloggers like this: