Tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na kasa Cif Olabode George, ya gargadi shugaba Bola Tinubu da ya yi tunani sosai kafin ya afkawa Jamhuriyar Nijar da yaki. A cikin wata wasika da yarubuta zuwa shugaban kasa a matsayinsa na “dan Najeriya, Janar mai ritaya a sojan Najeriya, mai kishin kasa kuma mai dabarar yaki,” George ya bayyana cewa yana da kyau shugaban ya ci gaba da harkokin diflomasiyya maimakon ya assasa “yakin da ba dole ba.”
Dattijon jamiyyar PDP Olabode George ya gargadi Tinubu kan yakar Nijar
Date:


