Connect with us

News in Hausa

Kotun sauraron kararrakin zabe a Kano sun fallasa yan siyasa

Published

on

Zarge-zargen da ke fitowa daga kotun sauraron kararrakin zaben ‘yan majalisar dokokin jihar Kano a baya-bayan nan na cewa wasu lauyoyi na neman yin tasiri ga alkalan da kudi a shari’o’i da dama da ke gabansu ya haifar da cece-kuce tare da zarge-zarge tsakanin jam’iyyu da masu ruwa da tsaki a fannin shari’a kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Yayin da kungiyar lauyoyin Najeriya NBA, ta rubutawa kotun bukatar ta akan ta bayyana musu sunayen mambobinta da ke da hannu a zarge-zargen cin hanci da rashawa, ta daya bangaren kuma manyan jam’iyyu biyu a jihar na ci gaba da musayar kalamai inda kowacce daga ciki ke nuna abokiyar hamayyar ta da yatsa inda kowacce ke zargin dayar nada hannu wajen badakalar cin hancin.

Jaridar The Boss ta tattaro cewa mai shari’a Flora Ngozi Azinge, shugabar kwamiti na 1 na kotun a zamanta na ranar Talata ta koka kan abin da ta bayyana a matsayin wani lamari mai tayar da hankali wanda a cikinsa lauyoyin da ke da kararrakin da ke gaban kwamitin na tuntubar ta da mambobin kwamitinta domin yin domin shawo kansu su karkarta kansu yayin yanke hukunci da kuma yin almundahana a shariar baki daya.

Amma babu tabbacin cewa sakatariyar kotun ta bayar ko taki bayar da cikakken bayani kan abin da ya faru a ranar Talata din. A yayin da ake ci gaba da shari’ar, mai shari’a Azinge ta yi wannan zargin ne a bayyana a gaban kotu…

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

News in Hausa

Kotu za ta yanke hukunci a kan zaben gwamnan Kaduna

Published

on

By

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ke jihar Kaduna za ta yanke hukunci a yau Alhamis 28 ga Satumba, 2023.
Jaridar The Boss ta samu labarin cewa kotun zata zartar da hukuncinta ne ta hanyar Zoom, a inda zata ayyana hukunci kan karar da jam’iyyar PDP da dan takararta, Isah Mohammed Ashiru Kudan suka gabatar a gabanta na neman korar Uba Sani a matsayin gwamnan jihar. Sani ya kasance dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a lokacin zaben.
Jaridar The Boss zata kawo cikakkun bayanai daga baya…

Continue Reading

News in Hausa

Kungiyar Kwadago Zata Shiga Yajin Aikin Sai Baba Tagani

Published

on

By

Kungiyoyin kwadago na NLC da TUC ta sanar da kudirinda na shiga aikin sai baba tagani a ranar Talata mai zuwa 3 ga watan Oktoba 2023. Hakan ya biyo bayan zaman tattaunawa da shugabannin kungiyoyin sukayi a yau Talata a Abuja.
Daya daga cikin korafin kungiyoyin nada alaka da halin tsananin wahala da yan Najeriya suke ciki, da kuma gazawar gwamnatin tarayya bisa alkawarin kawo tsare-tsare na rage radadi ga al’umma.

Continue Reading

News in Hausa

Gwamnan Kano Yusuf Na Jamiyyar NNPP Ya Daukaka Kara

Published

on

By

Gwamnan Jihar Kano, Alh Abba Kabir Yusuf da jamiyyar NNPP sun tafi kotun daukaka kara dake Kaduna domin daukakak kara kan hukuncin da kotun sauraren Korafe-Korafen Zaben gwamna a Jihar Kano ta Yanke a Bisa Kuskure.

Jaridar Boss ta tattaro bayani cewa gwamnatin Kano ta hayo manyan lauyoyi da zasu tsaya Mata a Kotun daukaka Kara da ke Kaduna.

Ga Jerin Gogaggun lauyoyin Masu Rike da Mukamin SAN ( Senior Advocate of Nigeria) Har Guda BAKWAI (7), Ga Jerin Sunayen Su Nan Akasa.

1. Chief Awomolo (SAN)
2. Chief John Beisha (SAN)
3. Chief Lawan Rabbana (SAN)
4. A . J Owonikoko (SAN)
5. Akomolafe (SAN)
6. Abdulhamid Muhammed (SAN)
7. Eyitayo Fatogun (SAN)

Continue Reading

Trending

%d bloggers like this: