Connect with us

News in Hausa

Dan majalisar tarayya, Bashir Gorau ya yunkura kan kawo karshen matsalar tsaro a Sokoto

Published

on

Hazikin matashin dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Goronyo da Gada da ke jihar Sokoto yayi wata ganawa da babban hafsan sojojin Najeriya Janar Taoreed Abiodun Lagbaja a yammacin yau Litinin.

Tattaunawar tasu dai tafi karkata kan yanda za a kawo karshen matsalar tsaro a wasu yankuna daga inda yake wakilta dama wasu sassan na jihar Sokoto baki daya, kamar yadda ya wallafa a shafukansa na kafafan sadarwa kamar haka:

“Nayi ganawa mai gamsarwa tare da babban Hafsan Sojojin kasa, Janar Taoreed Abiodun Lagbaja, inda muka tattauna hanyoyin magance matsalar rashin tsaro da ‘yan bindiga a Kananan Hukumomin Goronyo da Gada da kuma Sokoto ta Gabas baki ɗaya. Mun tattauna kafa sansanin Sojoji a Kwanar Mahalba, mazaunin Sojoji a Gada, da kuma shiga Dajin Gundumi domin kawarda ɓata-gari. Ina farin cikin cewa Janar Lagbaja ya himmatu wajen tabbatar da tsaronmu kuma yana neman goyon bayanmu, bayanai, da addu’o’in ga Sojoji domin samun nasarar wannan muhimmin aiki…”

Continue Reading
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

News in Hausa

Kotu za ta yanke hukunci a kan zaben gwamnan Kaduna

Published

on

By

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ke jihar Kaduna za ta yanke hukunci a yau Alhamis 28 ga Satumba, 2023.
Jaridar The Boss ta samu labarin cewa kotun zata zartar da hukuncinta ne ta hanyar Zoom, a inda zata ayyana hukunci kan karar da jam’iyyar PDP da dan takararta, Isah Mohammed Ashiru Kudan suka gabatar a gabanta na neman korar Uba Sani a matsayin gwamnan jihar. Sani ya kasance dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a lokacin zaben.
Jaridar The Boss zata kawo cikakkun bayanai daga baya…

Continue Reading

News in Hausa

Kungiyar Kwadago Zata Shiga Yajin Aikin Sai Baba Tagani

Published

on

By

Kungiyoyin kwadago na NLC da TUC ta sanar da kudirinda na shiga aikin sai baba tagani a ranar Talata mai zuwa 3 ga watan Oktoba 2023. Hakan ya biyo bayan zaman tattaunawa da shugabannin kungiyoyin sukayi a yau Talata a Abuja.
Daya daga cikin korafin kungiyoyin nada alaka da halin tsananin wahala da yan Najeriya suke ciki, da kuma gazawar gwamnatin tarayya bisa alkawarin kawo tsare-tsare na rage radadi ga al’umma.

Continue Reading

News in Hausa

Gwamnan Kano Yusuf Na Jamiyyar NNPP Ya Daukaka Kara

Published

on

By

Gwamnan Jihar Kano, Alh Abba Kabir Yusuf da jamiyyar NNPP sun tafi kotun daukaka kara dake Kaduna domin daukakak kara kan hukuncin da kotun sauraren Korafe-Korafen Zaben gwamna a Jihar Kano ta Yanke a Bisa Kuskure.

Jaridar Boss ta tattaro bayani cewa gwamnatin Kano ta hayo manyan lauyoyi da zasu tsaya Mata a Kotun daukaka Kara da ke Kaduna.

Ga Jerin Gogaggun lauyoyin Masu Rike da Mukamin SAN ( Senior Advocate of Nigeria) Har Guda BAKWAI (7), Ga Jerin Sunayen Su Nan Akasa.

1. Chief Awomolo (SAN)
2. Chief John Beisha (SAN)
3. Chief Lawan Rabbana (SAN)
4. A . J Owonikoko (SAN)
5. Akomolafe (SAN)
6. Abdulhamid Muhammed (SAN)
7. Eyitayo Fatogun (SAN)

Continue Reading

Trending

%d bloggers like this: