Hazikin matashin dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Goronyo da Gada da ke jihar Sokoto yayi wata ganawa da babban hafsan sojojin Najeriya Janar Taoreed Abiodun Lagbaja a yammacin yau Litinin.
Tattaunawar tasu dai tafi karkata kan yanda za a kawo karshen matsalar tsaro a wasu yankuna daga inda yake wakilta dama wasu sassan na jihar Sokoto baki daya, kamar yadda ya wallafa a shafukansa na kafafan sadarwa kamar haka:
“Nayi ganawa mai gamsarwa tare da babban Hafsan Sojojin kasa, Janar Taoreed Abiodun Lagbaja, inda muka tattauna hanyoyin magance matsalar rashin tsaro da ‘yan bindiga a Kananan Hukumomin Goronyo da Gada da kuma Sokoto ta Gabas baki ɗaya. Mun tattauna kafa sansanin Sojoji a Kwanar Mahalba, mazaunin Sojoji a Gada, da kuma shiga Dajin Gundumi domin kawarda ɓata-gari. Ina farin cikin cewa Janar Lagbaja ya himmatu wajen tabbatar da tsaronmu kuma yana neman goyon bayanmu, bayanai, da addu’o’in ga Sojoji domin samun nasarar wannan muhimmin aiki…”


