Dan majalisar tarayya, Bashir Gorau ya yunkura kan kawo karshen matsalar tsaro a Sokoto

Date:

Hazikin matashin dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Goronyo da Gada da ke jihar Sokoto yayi wata ganawa da babban hafsan sojojin Najeriya Janar Taoreed Abiodun Lagbaja a yammacin yau Litinin.

Tattaunawar tasu dai tafi karkata kan yanda za a kawo karshen matsalar tsaro a wasu yankuna daga inda yake wakilta dama wasu sassan na jihar Sokoto baki daya, kamar yadda ya wallafa a shafukansa na kafafan sadarwa kamar haka:

“Nayi ganawa mai gamsarwa tare da babban Hafsan Sojojin kasa, Janar Taoreed Abiodun Lagbaja, inda muka tattauna hanyoyin magance matsalar rashin tsaro da ‘yan bindiga a Kananan Hukumomin Goronyo da Gada da kuma Sokoto ta Gabas baki ɗaya. Mun tattauna kafa sansanin Sojoji a Kwanar Mahalba, mazaunin Sojoji a Gada, da kuma shiga Dajin Gundumi domin kawarda ɓata-gari. Ina farin cikin cewa Janar Lagbaja ya himmatu wajen tabbatar da tsaronmu kuma yana neman goyon bayanmu, bayanai, da addu’o’in ga Sojoji domin samun nasarar wannan muhimmin aiki…”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

spot_imgspot_img

Popular

More like this
Related

UK PM Burnham Unveils 10-Year Plan, Begins Cabinet Overhaul

The new British Prime Minister, Andy Burnham, on Monday,...

Where’s the Nigeria’s Oil Metering Fund?

By Boma Lilian Braide Esq A single administrative letter dated...

ADC Tells Tinubu to Resign As World Bank Reveals 139million Nigerians Live in Poverty

The African Democratic Congress (ADC) on Saturday asked President...

Dominican University Hails Peter Obi on 65th Birthday

The Dominican University, Ibadan, has paid glowing tribute to...