Gwamnatin mulkin soja ta Jamhuriyar Nijar ta yanke hulda da Najeriya bayan kokarin da kungiyar gamayyar kasashen yammacin Afirka ta ECOWAS ta yi na sasanta rikicin da ke faruwa ya ci tura.
Kungiyar ECOWAS ta ba da wa’adin kwanaki bakwai na maido da shugaban kasar Mohamed Bazoum kan mukaminsa domin kaucewa rikici da gwamnatin mulkin soji.


