Yayin da yake jawabi a taron manema labarai da jam’iyyarsa ta shirya a yau kan hukuncin kotun sauraron ƙorafin zaɓe da ta tabbatar da shugaba Bola Tinubu a matsayin halattaccen wanda ya lashe zaben shekara ta dubu biyu da uku da ya wakana a watan fabrairu, tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku, ya ce “har yanzu da sauran yaƙi”.
Kuma ya tabbatar wa da manema labarai cewa shi ba bako bane akan gwagwarmayar shari’a kuma yanada cikakken ilimi kan yanda kaidojin shari’a suke. Ya kuma umarci lauyoyinsa da suyi azama wajen shirye-shiryen cigar da kara a kotun koli domin kalubalantar ayyana Bola Tinubu a matsayin wanda yaci zabe da kotun sauraron kararrakin zaben tayi.


